Darussa daga Littafi Mai Tsarki

Wannan littafin zai sa ka san yadda Allah ya halicci abubuwa da yadda aka haifi Yesu da hidimar da ya yi da kuma yadda mulkin Allah zai zo.

Wasika Daga Hukumar da Ke Kula da Ayyukan Shaidun Jehobah

Ta yaya za a yin amfani da wannan littafin?

DARASI NA 1

Allah Ya Yi Sama da Duniya

Littafi Mai Tsarki ya ce Allah ya yi sama da duniya. Amma ka san mala’ikan da ya fara halitta kafin ya yi sauran abubuwa?

DARASI NA 2

Allah Ya Yi Mace da Miji na Farko

Allah ya yi mace da miji na farko kuma ya saka su a lambun Adnin. Za su iya haifan ’ya’ya kuma su mai da duniya gabaki daya aljanna.

DARASI NA 3

Adamu da Hauwa’u Sun Ki Bin Dokar Allah

Me ya sa itacen da ke tsakiyar lambun ya fita dabam? Me ya sa Hauwa’u ta ci daga ’ya’yan itacen?

DARASI NA 4

Fushi Ya Jawo Kisan Kai

Allah ya amince da hadayar Habila amma ya ki na Kayinu. Da Kayinu ya san da haka, sai ya yi fushi kuma ya yi zunubi.

DARASI NA 5

Jirgin Nuhu

Sa’ad da mala’iku suka auri mata a duniya, sun haifi manya-manyan yara masu mugunta sosai. Mugunta ta cika ko’ina. Amma Nuhu yana kaunar Allah kuma yana masa biyayya.

DARASI NA 6

Mutane Takwas Sun Tsira

An yi kwana 40 da dare 40 ana ruwan sama mai yawan gaske. Nuhu da kuma iyalinsa sun yi fiye da shekara daya a cikin jirgin. Daga karshe, sai Allah ya ce su fito.

DARASI NA 7

Hasumiyar Babel

Wasu mutane su ce za su gina babban gida wanda tsawonsa zai kai sama. Me ya sa Allah ya canja yarensu?

DARASI NA 8

Ibrahim da Saratu Sun Yi Biyayya ga Allah

Me ya sa Ibrahim da Saratu suka bar gidansu a birnin Ur kuma suka soma tafiya zuwa kasar Kan’ana?

DARASI NA 9

Sun Haifi Da!

Ta yaya Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim? A cikin yaran, wanne ne za a yi amfani da shi a cika wannan alkawarin?​—Ishaku ne ko kuma Isma’ilu?

DARASI NA 10

Ku Tuna da Matar Lutu

Allah ya yi amfani da wuta don ya halaka Saduma da Gwamarata. Me ya sa aka halaka wadannan biranan? Me ya sa ya kamata mu rika tunawa da matar Lutu?

DARASI NA 11

An gwada bangaskiyarsa

Allah ya gaya wa Ibrahim cewa: ‘Ka dauki yaro guda daya kawai da kake da shi, ka tafi kasar Moriah.’ Ta yaya Ibrahim zai bi da wannan yanayin?

DARASI NA 12

Yakubu Ya Sami Gādo

Ishaku da Rifkatu suna da ’yan biyu maza. Isuwa ne ya fara fitowa don hakan shi ne zai gaji gado na haihuwa. Amma me ya sa ya sayar wa Yakubu gadonsa saboda jar miya?

DARASI NA 13

Yakubu da Isuwa Sun Shirya

Ta yaya Yakubu ya sami albarka daga wurin mala’ika? Kuma ta yaya ya shirya da Isuwa?

DARASI NA 14

Wani Bawa da Ya Yi Biyayya ga Allah

Yusufu ya yi abin da ya dace amma duk da haka, ya sha wahala sosai. Me ya sa?

DARASI NA 15

Jehobah Bai Manta da Yusufu Ba

Duk da cewa Yusufu ya yi nesa da danginsa, Allah ya ci gaba da kasancewa tare da shi.

DARASI NA 16

Wane Irin Mutum Ne Ayuba?

Ya yi wa Jehobah biyayya duk da cewa hakan bai yi masa sauki ba.

DARASI NA 17

Musa Ya Bauta wa Jehobah

Sa’ad da Musa yake jariri, mahaifiyarsa ta cece shi don basirar da ta yi.

DARASI NA 18

Bishiya Mai Cin Wuta

Me ya sa wutar ba ta cinye bishiyar ba?

DARASI NA 19

Annoba ta Daya Zuwa Uku

Fir’auna janyo annoba wa mutanensa saboda da fahariyarsa bai kyale shi ya yi abin da ya kamata ya yi ba.

DARASI NA 20

Annoba ta Hudu Zuwa Tara

Mene ne bambancin da ke tsakanin annobar nan da sauran guda ukun?

DARASI NA 21

Annoba ta Goma

Wannan annobar ta yi muni sosai, har ta sa Fir’auna da kansa ya yi biyayya.

DARASI NA 22

Abu Mai Ban Mamaki a Jar Teku

Annoba guda goma ba su kashe Fir’auna ba, amma wannan mu’ujizar da Allah ya yi ya kashe shi.

DARASI NA 23

Sun Yi wa Jehobah Alkawari

Sa’ad da Isra’ilawa suka zo dutsen Sinai, sun yi wa Allah alkawari a wajen.

DARASI NA 24

Ba Su Cika Alkawarinsu Ba

Yayin da Musa ya je karban Dokoki Goma, sai mutanen suka yi zunubi.

DARASI NA 25

Mazauni don Ibada

Wannan tantin yana dauke da akwatin alkawari.

DARASI NA 26

’Yan Leken Asiri

Joshua da Kaleb sun bambanta da sauran maza goman da suka je leken asiri a Kan’ana.

DARASI NA 27

Sun Yi wa Jehobah Rashin Biyayya

Korah da Dathan da Abiram da kuma mutane guda 250 sun ƙi su fahimci wani abu game da Jehobah.

DARASI NA 28

Jakin Balaam Ya Yi Magana

Jakin ya ga wani abu da Balaam bai iya gani ba.

DARASI NA 29

Jehobah Ya Zabi Joshua

Dokokin da Allah ya ba Joshua za su iya taimaka mana a yau.

DARASI NA 30

Rahab Ta Boye ʼYan Leken Asiri

Katangar Yariko ta rushe gabaki daya. Amma gidan Rahab bai rushe ba duk da cewa gidan hade yake da katangar.

DARASI NA 31

Joshua da Gibeyonawa

Joshua ya roki Allah: “Rana ta tsaya cak!” Shin Allah ya amsa wannan addu’ar?

DARASI NA 32

Sabon Shugaba da Mata Biyu Masu Karfin Zuciya

Isra’ilawa sun soma bautar gumaka bayan Joshua ya mutu. Sun sha wahala sosai. Amma Jehobah ya yi amfani da Alkali Barak da annabiya Deborah da kuma Jael don ya cece su!

DARASI NA 33

Ruth da Naomi

Wadannan mata biyu da mazansu sun rasu sun koma Isra’ila. Daya daga cikinsu mai suna Ruth ta je aiki a wani gona. A gonar ce Boaz ya hadu da ita.

DARASI NA 34

Gidiyon Ya Ci Midiyanawa da Yaki

Isra’ilawa sun roki Jehobah ya taimaka musu bayan Midiyanawa sun wahalar da su sosai. Ta yaya sojojin Gidiyon guda 300 suka ci sojojin Midiyanawa guda 135,000 a yaki?

DARASI NA 35

Hannatu Ta Roki Allah Ya Ba Ta Yaro

Elkanah ya kai Hannatu da Peninnah, da kuma yaransa bauta a mazaunin da ke Shiloh. A nan ne Hannatu ta roki Allah ya ba ta yaro. An haifi Sama’ila bayan shekara daya!

DARASI NA 36

Alkawarin da Jephthah Ya Yi

Wane alkawari ne Jephthah ya yi, kuma me ya sa? Ta yaya ʼyar Jephthah ta ji don alkawarin da babanta ya yi?

DARASI NA 37

Jehobah Ya Yi Magana da Sama’ila

Yaran Eli Babban Firist guda biyu suna hidima a mazaunin, amma ba su yi biyayya ga dokokin Allah ba. Sama’ilawa wanda shi matashi ne bai bi halinsu ba, kuma Jehobah ya yi masa magana.

DARASI NA 38

Jehobah Ya Ba Samson Karfi

Allah ya sa Samson karfi sosai domin ya rika yaki da Filistiyawa. Amma sa’ad da ya yanke shawara marar kyau, Filistiyawa sun kama shi.

DARASI NA 39

Sarki Na Farko a Isra’ila

Allah ya ba wa Isra’ilawan alkalai don su ja-gorance su amma mutanen su ce sarki suke so. Sama’ila ya nada Saul a matsayin sarki na farko amma Jehobah ya ki shi daga baya. Me ya sa?

DARASI NA 40

Dauda da Goliath

Jehobah ya zabi Dauda ya zama sarkin Isra’ila, kuma Dauda ya nuna dalilin da ya sa ya cancanci ya zama sarki.

DARASI NA 41

Dauda da Saul

Me ya sa Saul ya tsane Dauda kuma wane mataki ne Dauda ya dauka?

DARASI NA 42

Jonathan Mai Karfin Hali da Aminci

Yaron sarki ya zama abokin Dauda.

DARASI NA 43

Zunubin Sarki Dauda

Shawara marar kyau tana kawo matsaloli.

DARASI NA 44

Haikalin Jehobah

Allah ya amince da addu’ar Sarki Sulemanu kuma ya albarkace shi sosai.

DARASI NA 45

An Raba Mulkin

Isra’ilawa da yawa sun daina bauta wa Jehobah.

DARASI NA 46

Jehobah Ne Allah Na Gaskiya

Wane ne Allah Na Gaskiya? Jehobah ko Baal?

DARASI NA 47

Jehobah Ya Karfafa Iliya

Shin Jehobah zai iya karfafa ka?

DARASI NA 48

Yaron Wata Gwauruwa Ya Tashi Daga Mutuwa

An yi mu’ujiza guda biyu a wani gida!

DARASI NA 49

An Hukunta Wata Muguwar Sarauniya

Jezebel ta yi shiri a kashe wani dan Isra’ila mai suna Naboth don ta kwace gonarsa! Amma Jehobah ya ga kulle-kullen da ta yi kuma ya hukunta ta.

DARASI NA 50

Jehobah Ya Kāre Jehoshaphat

Sa’ad da makiya suke so su kai wa Yahuda hari, sarki Jehoshaphat ya roki taimakon Allah.

DARASI NA 51

Wani Mayaki da Kuma Wata Yarinya

Wata karamar yarinya yar Isra’ila ta gaya wa uwar gidanta game da ikon Jehobah kuma hakan ya sa abin al’ajabi ya faru.

DARASI NA 52

Dawaki da Karusan Wuta na Jehobah

yadda aka nuna wa bawan Elisha cewa ‘wadanda suke tare da mu sun fi nasu.’

DARASI NA 53

Jehoiada Ya Yi Karfin Hali

Wani firist mai aminci ya yaki wata muguwar sarauniya.

DARASI NA 54

Jehobah Ya Yi Hakuri da Yunana

Ta yaya babban kifi ya hadiye wani annabin Allah? Ta yaya ya fito daga cikin kifin? Kuma wane darasi ne Jehobah ya koya masa?

DARASI NA 55

Mala’ikan Jehobah Ya Kāre Hezekiya

Makiyan Yahudawa sun ce Jehobah ba zai kāre mutanensa ba amma hakan ba gaskiya ba ne!

DARASI NA 56

Josiah Yana Son Dokar Allah

Josiah ya zama sarki sa’ad da yake dan shekara takwas kuma ya taimaka wa mutanensa su soma bauta wa Jehobah.

DARASI NA 57

Jehobah Ya Aiki Irmiya Ya Yi Wa’azi

Abin da wannan annabin ya ce ya ba wa dattawan Yahuda haushi sosai.

DARASI NA 58

An Halaka Urushalima

Mutanen Yahuda sun ci gaba da bauta wa allolin karya, don haka Jehobah ya rabu da su.

DARASI NA 59

Matasa Hudu da Suka Yi wa Jehobah Biyayya

Wadannan matasa Yahudawan sun kudurta za su rike amincinsu ga Jehobah ko a Babila.

DARASI NA 60

Gwamnatin da Za ta Yi Sarauta Har Abada

Daniyel ya bayyana ma’anar mafarkin Nebuchadnezzar.

DARASI NA 61

Sun Ki Bauta wa Gunki

Shadrach da Meshach da kuma Abednego su ki bauta wa gunki zinariya da sarkin Babila ya yi.

DARASI NA 62

Mulkin da Ke Kama da Babbar Bishiya

Mafarkin Nebuchadnezzar game da kansa ne.

DARASI NA 63

Rubutu a Jikin Bango

Me ya sa rubutu ya bayyana, kuma mene ne rubutu yake nufi?

DARASI NA 64

An Saka Daniyel a Cikin Ramin Zakuna

Kamar yadda Daniyel ya yi, ka rika yi wa Jehobah addu’a a koyaushe!

DARASI NA 65

Esther Ta Ceci Mutanenta

Ta zama sarauniya duk da cewa ita ba ’yar kasar Fasiya ba ce kuma ba ta da iyaye.

DARASI NA 66

Ezra ya koyar da Dokar Allah

Bayan mutanen sun saurari abin Ezra ya gaya musu, sai suka yi alkawari na musamman wa Allah.

DARASI NA 67

Ganuwar Urushalima

Me ya sa Nehemiya bai ji tsoro ba sa’ad da ya ji cewa makiyansa suna sun su kawo masa hari?

DARASI NA 68

Alisabatu Ta Haifi Yaro

Me ya sa mala’ikan ya gaya wa Zakariya cewa ba zai iya yin magana ba har sai an haifi yaron?

DARASI NA 69

Mala’ika Jibra’ilu Ya Ziyarci Maryamu

Ya gaya mata sakon da zai canja yanayin rayuwarta.

DARASI NA 70

Mala’iku Sun Sanar da Haihuwar Yesu

Mala’ikun da suka ji sakon sun dauki mataki nan da nan.

DARASI NA 71

Jehobah Ya Kāre Yesu

Wani mugun sarki yana so ya kashe Yesu.

DARASI NA 72

Sa’ad da Yesu Yake Karami

Me ya sa malamai a haikalin suka yi mamakin sa?

DARASI NA 73

Yohanna Ya Shirya wa Yesu Hanya

Yohanna ya zama annabi sa’ad da ya girma. Ya gaya wa mutane game da zuwan Almasihu. Mene ne mutane suka yi sa’ad da suka ji haka?

DARASI NA 74

Yesu Ya Zama Almasihu

Me ya sa Yohanna ya ce Yesu shi ne Dan Rago na Allah?

DARASI NA 75

Shaidan Ya Jarraba Yesu

Shaidan ya jarraba Yesu sau uku. Wadanne abubuwa uku ne ya yi amfani da su don ya jarraba shi? Mene ne Yesu ya yi?

DARASI NA 76

Yesu Ya Tsabtacce Haikalin

Me ya sa Yesu ya dauki bulala kuma ya kori dabbobin da ke haikalin da kuma ture teburan masu canjin kudi?

DARASI NA 77

Yesu da Wata Mata a Bakin Rijiya

Basamariyar da ke kusa da rijiyar Yakubu ta yi mamaki sa’ad da Yesu ya yi mata magana. Me ya sa? Mene ne Yesu ya gaya mata da bai taba gaya wa kowa ba?

DARASI NA 78

Yesu Ya Yi Wa’azi Game da Mulkin Allah

Yesu ya gaya wa wasu mabiyansa su zama masu kama mutane. Bayan wasu lokaci, ya horar da mabiyansa guda 70 don su yi wa’azi.

DARASI NA 79

Yesu Ya Yi Mu’ujizai da Yawa

Duk inda Yesu ya je, marasa lafiya suna zuwa wurinsa don ya taimaka musu kuma ya warkar da su. Har ma ya ta da wata yarinya daga mutuwa.

DARASI NA 80

Yesu Ya Zabi Manzanni Goma Sha Biyu

Me ya sa ya zabe su? Ka san sunansu?

DARASI NA 81

Koyarwa a Kan Dutse

Yesu yana koyar wa taron jama’a wasu muhimman darussa.

DARASI NA 82

Yesu Ya Koya wa Almajiransa Yin Addu’a

Mene ne Yesu ya gaya wa mabiyansa su rika addu’a kai?

DARASI NA 83

Yesu Ya Ciyar da Dubban Mutane

Mene ne mu’ujizar da Yesu ya yi ya koya mana game da Yesu da kuma Jehobah?

DARASI NA 84

Yesu Ya Yi Tafiya a Kan Teku

Ka yi tunanin yadda manzannin suka ji sa’ad da suka ga wannan mu’ujiza

DARASI NA 85

Yesu Ya Yi Warkarwa a Ranar Assabaci

Me ya sa mutane ba sa son abin da yake yi?

DARASI NA 86

Yesu Ya Tayar da Li’azaru Daga Matattu

Da Yesu ya ga Maryamu tana kuka, sai shi ma ya soma kuka. Amma daga bayan, sun daina kuka kuma suka soma farin ciki.

DARASI NA 87

Idin Ketarewa na Karshe da Yesu Ya Yi

Yesu ya koya wa mabiyansa wani darasi mai muhimmanci a lokacin da yake yin idi na karshe.

DARASI NA 88

An Kama Yesu

Yahuda ya zo da sojoji rike da makamai don su kama Yesu.

DARASI NA 89

Bitrus Ya Yi Musun Sanin Yesu

Mene ne ya faru a gidan Kayafa? Mene ne aka yi wa Yesu a gidan Kayafa?

DARASI NA 90

Yesu Ya Mutu a Golgota

Me ya sa Ba-bunti ya ce a kashe Yesu?

DARASI NA 91

Allah Ya Tayar da Yesu Daga Matattu

Wadanne abubuwan ban mamaki ne suka faru bayan an kashe Yesu?

DARASI NA 92

Yesu Ya Je Wajen Masu Kama Kifi

Mene ne Yesu ya yi don ya jawo hankalinsu wurinsa?

DARASI NA 93

Yesu Ya Koma Sama

Kafin ya koma sama, ya ba wa almajiransa shawarwari masu kyau.

DARASI NA 94

An Ba Mabiyan Yesu Ruhu Mai Tsarki

Wani abu ne ruhu mai tsarkin ya taimaka musu su yi?

DARASI NA 95

Sun Ki Su Daina Wa’azi

Malaman addinai da suka sa aka kashe Yesu suna son su hana mabiyansa yin wa’azi. Amma ba za su iya ba.

DARASI NA 96

Yesu Ya Zabi Shawulu

Bulus ya tsani Kiristoci, amma ra’ayinsa ya kusan canjawa.

DARASI NA 97

Karniliyus Ya Sami Ruhu Mai Tsarki

Me ya sa Allah ya aika Bitrus zuwa gidan wannan mutumin da ba Bayahude ba?

DARASI NA 98

Mutane da Yawa Sun Zama Kiristoci

Manzo Bulus da abokansa sun soma wa’azi a kasashe masu nisa.

DARASI NA 99

Wani Mai Gadi Ya Zama Kirista

Ta yaya aljani da girgizar kasa da kuma takobi suka shafi wannan labarin?

DARASI NA 100

Bulus da Timotawus

Su biyu sun yi shekaru da yawa suna aiki tare

DARASI NA 101

An Tura Bulus Kasar Roma

Tafiyar da suka yi na cike da hatsari, amma babu abin da ya isa ya hana wannan manzon yin hidimarsa.

DARASI NA 102

Wahayin da Aka Saukar wa Yohanna

Yesu ya saukar masa da wahayoyi game da nan gaba.

DARASI NA 103

Bari “Mulkinka Ya Zo”

Wahayin da Yohanna ya gani ya nuna yadda Mulkin Allah zai canja yanayinmu a duniya.